– Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana
‘Yan Kungiyar IMN a matsayin ‘yan tawaye
– Gwamnati tace za ta hukunta Shugaban Kungiyar Ibrahim El-Zakzaky
– Za a kama El-Zakzaky da laifin mabiyan sa
Ta
tabbata cewa Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana Kungiyar IMN a matsayin ‘yan
tawaye. Wannan yana cikin bayanin da Gwamnatin Jihar ta fitar da shi bayan
bincike da aka gudanar na dogon lokaci.
Takardar
da aka fitar jiya ta bayyana cewa ‘Yan Kungiyar IMN din ‘yan tawaye ne masu
tada zaune-tsaye don haka dole a dauki mataki game da su. Haka kuma takardar ta
nuna cewa dole a Hukunta Ibrahim El-Zakzaky.
Takardar
da Gwamnatin Tarayya ta fitar ya nuna cewa ‘Yan Kungiyar IMN din suna bin
El-Zakzaky dari-bisa-dari, hakan ta sa ya kamata a kama sa da duk laifin da
suka aikata. A rikicin Shi’ar da Soji da ya faru a bara, an hallaka ‘yan shi’a
fiye da 300 a Garin. Gwamnatin Jihar tace za ta bar Gwamnatin Tarayya ta
Hukunta Sojojin da ke da laifi.
Shugaban
Kungiyar ta IMN, Ibrahim Yakub El-Zakzaky yana can a daure, kwanan ne dai wani
Babban Kotu ya bada izinin a sake sa da gaggawa.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment