Thursday, December 29, 2016

An koma cin naman kare a Ekiti


Jama’a sun komawa naman kare a Jihar Ekiti


Duk inda ka je kurum da naman kare ake dagargajewa


Ana sayar da karnuka 'yan wata uku N500




Yanzu haka Karnuka sun fara bacewa a Jihar Ekiti, domin kuwa duk inda ka shiga cin abinci sai dai ka ga naman kare a cikin miya. Mutanen Jihar Ekiti dai sun komawa naman karnuka. Hukumar Dillacin labarai na Kasa ta bada wannan labari.

A Garuruwa irin su Ise-Ekiti, Ado-Ekiti, Ikere-Ekiti da sauran su naman Karen ya zama wani kayan Gabas, ko ina rububin kare ake yi. A gidaje da wuraren cin abinci ma da Gidan ruwa, ko ina kare kurum ake babbakawa ba kama hannun yaro.

Yanzu haka har farfesun kare ake yi a wasu wuraren.  Abin dai har ta kai babu karnuka a kan titi, don kuwa tuni sun shige tukunya. A na sayar da jariran karnuka a kan N500, manya kuma su kan kai har N15000; ain dai, iya kudin ka, iya shagalin ka.

A watan Agusta Gwamna Fayose na Jihar ya sa hannu kan wata doka da ta haramta kiwon shanu da sauran dabbobin noma a Jihar, Dokar tace duk wanda aka kama ya saba doka, za a daure sa na rabin shekaru kuma babu damar karbar tara. Dokar ta haramta kiwo daga karfe 6 na yamma har zuwa 7 na safe. Sai dai masana sun ce naman kare yana da illa kwarai a jikin Dan Adam.


 [NAIJ Hausa]



No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...