Thursday, December 15, 2016

Sanatoci sun hurowa Sakataren Gwamnati wuta






– ‘Yan Majalisar Dattawan Kasar nan sun nemi Sakataren Gwamnatin Shugaba Buhari ya sauka daga matsayin sa 

 



Wani bincike da Majalisar tayi, ya nuna cewa Babachir David ba shi da gaskiya

 



Sakataren Gwamnatin yana cikin wadanda suka yi gaba da kudin ‘Yan Gudun Hijira da ke Arewa maso Gabas


A zaman ‘Yan Majalisar Dattawan Kasar nan jiya, sun amince cewa lallai Sakataren Gwamnatin na Tarayya ya sauka daga mukamin sa. Majalisar Dattawan ta bayyana cewa ta gano Babachir David Lawal ya mikawa kan sa wasu Kwangila domin ‘Yan gudun Hijira na Yankin. 

Wani bincike da Sanata Shehu Sani yayi ya nuna cewa Kamfanin su Babachir sun samu kwangilar Miliyoyi da aka tsulawa kudi a Yankin da rikicin Boko Haram ya shafa. Wani Kamfanin su Babachir aka ba kwangilar aske ciyayi har na sama da Miliyan 200 a Jihar Yobe. 

Sanata Melaye yace sai dai Sakataren yayi wuf ya cire sunan sa daga cikin masu mallakar Kamfanin. Amma Majalisar tace ta bincika ta gano cewa lallai har yanzu Babachir din yana da hannu a Kamfanin. 

An nemi Babachir ya sauka daga matsayin, domin a bincike sa, kuma a hukunta sa. Sakataren Gwamnatin dai yace ana kokarin bata masa suna ne kurum.


Muhammad Malumfashi ya fassara wannan a NAIJ Hausa

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...