– Ana ta samun rade-radin cewa Shugaban Kasa ya sauke Hafsun Sojin Kasar
– Shugaban Kasar yace karya ce kurum ake ta yadawa
– Sai dai kuma Shugaban Hafsun Sojojin Kasar zai ajiye aiki mako mai zuwa
Mai magana da yawun Shugaban
Kasar, Femi Adesina yace maganar cewa Shugaba Buhari ya sauke Hafsun Sojin
Kasar ba gaskiya bane. Femi Adesina yace an kara gishiri a cikin asalin yadda
lamarin yake.
Femi Adesina wanda shine ke
ba Shugaban Kasa Muhammadu Buhari shawara game da harkokin yada labarai, yace a
maimakon Jaridar su shiga yada labarai na karya, da sun bincika, sun ji yadda
maganar ta ke.
An rahoto cewa Shugaba
Buhari ya sauke Janar Olanishakin wanda shine Shugaban Hafsun Sojojin Najeriya
da kuma Admiral Ibok-Ete Ekwe Ibas watau Hafsun Sojin ruwa. Sai dai Shugaban
Kasan ya bayyana yadda abin yake.
Femi Adesina ya ce shekarun
Janar Olanishakin na aiki sun cika, don haka zai ajiye aiki. Shi kuwa Admiral
Ibok-Ete Ekwe Ibas har yanzu da sauran shekarun aiki a gaban sa, don haka yana
nan. Amma Janar Olanishakin zai yi ritaya mako mai zuwa, kuma har yanzu ba a
fadi wanda zai maye gurbin sa ba.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment