Friday, December 30, 2016

NAFDAC tayi gargadi game da shinkafar roba


Hukumar NAFDAC ta gargade ‘Yan Najeriya da cin shinkafar nan ta roba


Shinkafar ba ta da Rajistar NAFDAC


Wannan Shinkafa dai na da illa ga lafiyar mutum




Hukumar kula da Abinci da Magunguna a Kasar nan watau NAFDAC ta gargadi Jama’a da su bi a hankali da Shinkafar nan da ake cewa ta roba. Hukumar tace asalin Shinkafar ba wai ta roba ba ce, sai dai gurbataciyya.

Hukumar ta ce har wa yau, wannan Shinkafa ba ta da ragistar NAFDAC da sauran bayanai da ke nuna daga inda Shinkafar ta fito. Shugaban Hukamar NAFDAC din mai kula da magunguna da Abinci, Yetunde Oni tace bai dace a rika cin irin wannan Shinkafa ko wanin sa ba.

NAFDAC din ta bayyana cewa za a kona irin wadannan Shinkafa da Hukumar kwastam ta Najeriya ta karbe. A wani Bincike da Hukumar tayi a Dakin taro, an gano matsaloli tattare da kwayar shinkafar.

Yayin da Kirismetin nan ya zo kuma, Mutane da dama sun shiga neman shinkafar gida a Najeriya. Wurare irin su Cross-River abin ba a cewa komai don kuwa kowa na neman shinkafar biki mai dan araha. Hukumar Dillacin Labarai ta dauko wannan rahoto daga Calabar. Wani daga cikin mazauna yankin yace shinkafar gida ta fi araha, kuma ga dadi.




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...