– Hukumar
NAFDAC ta gargade ‘Yan Najeriya da cin shinkafar nan ta roba
– Shinkafar ba ta da Rajistar NAFDAC
– Wannan
Shinkafa dai na da illa ga lafiyar mutum
Hukumar kula da Abinci da
Magunguna a Kasar nan watau NAFDAC ta gargadi Jama’a da su bi a hankali da
Shinkafar nan da ake cewa ta roba. Hukumar tace asalin Shinkafar ba wai ta roba
ba ce, sai dai gurbataciyya.
Hukumar ta ce har wa yau,
wannan Shinkafa ba ta da ragistar NAFDAC da sauran bayanai da ke nuna daga inda
Shinkafar ta fito. Shugaban Hukamar NAFDAC din mai kula da magunguna da Abinci,
Yetunde Oni tace bai dace a rika cin irin wannan Shinkafa ko wanin sa ba.
NAFDAC din ta bayyana cewa
za a kona irin wadannan Shinkafa da Hukumar kwastam ta Najeriya ta karbe. A
wani Bincike da Hukumar tayi a Dakin taro, an gano matsaloli tattare da kwayar
shinkafar.
Yayin da Kirismetin nan ya
zo kuma, Mutane da dama sun shiga neman shinkafar gida a Najeriya. Wurare irin
su Cross-River abin ba a cewa komai don kuwa kowa na neman shinkafar biki mai
dan araha. Hukumar Dillacin Labarai ta dauko wannan rahoto daga Calabar. Wani
daga cikin mazauna yankin yace shinkafar gida ta fi araha, kuma ga dadi.
No comments:
Post a Comment