Saturday, December 10, 2016

Samari fiye da 14,000 suke fama da Kanjamau a Benue

– Dubunnan Samari ke dauke da kwayar cutar Kanjamau a Jihar Benue

 

Bincike ya nuna cewa matasa sama da 14,000 ke tare da wannan mugun cuta

 

Shugaban masu Kanjamu ya bayyana haka

 

Shugaban Kungiyar masu cutar Kanjamau ya bayyana cewa samari da ‘yan mata fiye da 14,000 ke fama da cuta Kanjamau-watau HIV/AIDS a Jihar Benue. Shugaban masu Kanjamau din ya bayyana haka ne wannan makon a Garin Makurdi.

Shugaban masu Cutar sida yayi wannan jawabi ne a Ranar Kanjamau ta Duniya wanda aka yi kwanan nan. Yake cewa abin yayi yawa kwarai, Shugaban yake cewa ana shirin samar da magunguna ga ‘Ya ‘yan Kungiyar domin kawo saukin cutar.

Shugaban Kungiyar, Fabian Tor yace idan aka samu magani, shi zai kawo sauki ga masu cutar. Darektan Kungiyar UNAIDS na Cutar Kanjamau a Kasar, Dr. Camara Bilali yace Jihar Benue na cikin Jihohin da suka fi kowa fama da cutar Kanjamau. 

Kungiyar UNAIDS ta Majalisar Dinkin Duniya mai kula da Kanjamau tace ya zama aikin mu gaba daya mu tashi tsaye wajen yakar wannan cuta. Kwanan ne a aka gano cewa mutane kusan 10,000 ke dauke da kwayar cutar ta Kanjamau a Jihar Legas.


[NAIJ Hausa]







No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...