Saturday, December 24, 2016

Gambia: Za a karbe mulki da karfi da yaji



– Ana shirin tunbuke Shugaban Kasar Gambia babu girma, ba arziki



– Kungiyar ECOWAS tace ta tanadi Sojojin da za su kutsa Gambia



Sojojin Najeriya ne dai kan gaba




Kwanakin baya ne Shugaban Kasar Gambia ya sanar a Gidan Talabiji cewa ba abin da zai sa ya sauka daga Shugabancin Kasar. Karshen makon jiya  ne Shugaba Buhari da wasu Shugabannin Afrika su ka kai ziyara Kasar domin ganin Shugaba Jammeh ya amince da sakamakon zaben da ya sha kashi.

Sai dai Shugaba Jammeh yace ziyarar da su Buhari suka kai bai canza komai ba. Yace babu dalilin da zai sa ya sauka daga mulkin Kasar. Don haka Kungiyar ECOWAS na shirya bataliya guda na Sojoji da za su kutsa Kasar su ga cewa an sauke Shugaba Jammeh da karfin tsiya.

Premium Times tace Marcel de Souza na Kungiyar ECOWAS ke cewa idan har wa’adin Shugaba Jammeh ya cika, bai sauka ba, za a bi ta karfi da yaji a tunbuke sa ba girma ba arziki. Sojojin Najeriya ne dai kan gaba cikin Rundunar da aka tanada masu shiga Kasar. An dai san Sojin Najeriya da kokari a Nahiyar.

Shugaban Kasar Jammeh, yayi amai ya lashe game da sakamakon zaben. Shugaba Jammeh ya fi shekara 20 yana mulkin Kasar Gambia.

 


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...