– Wata Budurwa mai suna Saudah ta
auri dan wasan Najeriya
– Saudah ta auri Musa Yahata, wanda ya bugawa Najeriya
tamola
– An
yi auren ne a Garin Kaduna
A wannan makon ne dai aka
daura auren Musa Yahaya da Amaryar sa Hajiya Saudah. Musa Yahaya Dan wasan
Kwallon Kafa ne wanda ya bugawa Najeriya a mataki na samartaka dabam-dabam.
Musa ya bugawa Najeriya
Gasar ‘Yan wasan Kasa da shekaru 17 watau U- 17 da kuma U-20.
Sannan Musa ya wakilci Kasar nan a Gasar Olympics na masu shekaru kasa da 23.
Dan wasa Musa Yahaya dai yanzu haka yana taka leda ne a kasar Portugal ta
Turai.
An dai daura wannan aure ne
a Kaduna. Manyan Taurarin ‘Yan wasa irin su Lukman Zakari, Sulaiman watau
‘Daddy’, Alfa Abdullahi da Kocin Dan wasan Manu Garba da sauran Jama’a suka
halarci wannan Biki.
Ko da yake dai ana cewa
Amaryar Saudah, ‘Yar wasan kwaikwayo ce, da alamu ta musanya wannan magana.
Tana dai sha’awar kwallon kafa kamar yadda ta bayyana.
Allah ya ba su zaman lafiya…
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment