– Wani Dan Majalisa ya kawo kudirin kafa Kotun Kirista a Najeriya
– Yanzu har wannan kudiri ya tsallake mataki na biyu
– Hon. Gyang Dung na mazabar Plateau ya kawo wannan kudiri
Wani Dan Majalisa Wakilai ta
Tarayya mai suna Hon. Gyang Dung daga Jihar Plateau ya kawo wani kudiri zuwa
Majalisar Kasar inda yake nema a kafa Kotun Kirista a fadin Kasar nan. Watau
dai wannan zai yi daidai da kamar Kotun Shari’ah na Musulunci.
Yanzu dai haka wannan kudiri
na kafa Kotun Ikilisiya ya samu tsallake mataki na biyu a Fadar Majalisar. Hon.
Gyang Dung na PDP da ke wakiltar mazabar Plateau ne ya gabatar da kudirin tare
da wasu ‘Yan Majalisa 8.
Dan Majalisan yace idan har
an kafa wannan Kotu, za ta zama tana aiki musamman ga abubuwan da suka shafi
Addinin Kirista. Hon. Dung ya bayyanawa manema labarai cewa Kotun ba za tayi
aiki a kan wanda bai yadda da Ikiliziya da Addinin Kirista ba.
Sai anyi wa dokar Kasar nan
garambawul dai kafin a shigar da wannan kudiri cikin dokar tsarin mulkin Kasa.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment