Tuesday, December 13, 2016

Tofa: Za a binciki Shugaba Buhari



– ‘Yan Majalisar Dattawan Kasar nan za su fara binciken kudin mai da suka bace a Gwamnatin Shugaba Buhari

 



Ana zargin NNPC ta sha kwana da wasu Dala Biliyan 6.9

 



An dai saba sace kudin man Kasar ta asusun NNPC

 

 

 
A zaman ‘Yan Majalisar Dattawan Kasar nan sun amince cewa lallai za a binciki wasu kudi da suka bata a Gwamnatin Shugaba Buhari. Majalisar tace bai kamata wasu kudi su rika bacewa daga asusun Gwamnatin ba yayin da ake fama da rashin kudi a Kasar.

Sanata Dino Melaye ne ya kawo kudirin cewa ya kamata a duba wannan batu, Sanata Ali Ndume; Shugaban masu rinjaye a Majalisar kuwa ya mara masa baya. Sanatan yace kudi kusan  Dalan Biliyan 7 sun yi kafa daga NNPC da kuma NPDC. 

Majalisar za ta binciki Shugaba Buhari da kuma Ma’aikatar mai; Dr. Ibe Kachikwu da kuma Shugaban Kamfanin mai na Kasar watau NNPC; Maikanti Baru. Majalisar Dattawar kuma za ta binciki Gwamnan Babban Bankin Kasar; Godwin Emefiele. 

Shugaban Majalisar Dattawar, Abubakar Bukola Saraki yace wasu na kokarin ganin yaki da cin hanci da rashawan da wannan Gwamnati ta ke yi bai kai ga ci ba.

[NAIJ Hausa]


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...