– Janar TY Buratai yace so samu kowane Soja ya koma Bariki a shekara mai zuwa
– Hafsun Sojin Kasar yace an kusa kawo karshen Boko Haram
– Janar Buratai yayi alkawarin sauya Sojojin da ke filin daga a kan kari
Hafsun Sojin Kasa na Najeriya, Laftana-Janar Tukur Buratai yace zuwa shekarar 2017 Sojojin Kasar nan da ke fada da ‘Yan Boko Haram za su koma bariki. Janar Buratai yace yakin ya kusa zuwa karshe.
Janar Buratai yace idan so samu ne, zuwa badi kowane Soja
ya koma gida. Shugaban Sojojin Kasan yayi wannan magana ne lokacin da ya
ziyarci Rundunar Sojin Kasar a Ranar Litinin. Kwanan nan ne dai Bam suka yi ta
tashi a Arewa-maso-Gabas.
Buratai yace dole zuwa karshen Disamban nan su gama
lallasa ‘Yan Boko Haram da suka rage a Kasar. Janar din yace yayi alkawarin
Soji da yawa za su koma gidajen su shekara mai zuwa. Buratai yace za a riga
canza Sojojin da ke bakin daga bayan watanni 6, kuma yayi alkawarin sakin kudin
su a kai-a kai.
Jiya ne kuma Mai magana da yawun Shugaban Kasar, Femi Adesina yace
maganar cewa Shugaba Buhari ya sauke wasu Hafsun Sojin Kasar ba gaskiya bane.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment