– Yayin da Sambisa ta fadi daga hannun ‘Yan Boko Haram sai ga Abubakar Shekau ya bayyana
– Abubakar Shekau yace Rundunar
Sojin Najeriya karya take yi
– Shekau yace ba dai mutum ba sai
Ubangiji
A
jiya ne aka sanu wani sabon Bidiyo na Abubakar Shekau na Boko Haram inda yake
karyata maganar Sojin Najeriya na cewa an fatattake su watau Boko Haram daga
Sambisa. Shekau ya bayyana abubuwa da dama a sakon na sa, kamar haka:
1. Karyar banza ce ace an fatattaki ‘Yan Boko Haram.
2. Ubangiji ne kadai ke da iko a kan su ba Sojin
Najeriya ba.
3. Shekau yace karfi ba a bakin Bindiga ta ke ba, sai
dai mai Duka.
4. Maganar cewa an kama ‘Yan Boko Haram har fiye da 1200
karyar banza ce.
5. Shekau ya gargadi Kasashen Duniya irin su Jamus,
Faransa, Italiya da sauran su.
6. Shekau ya kara sukar tsarin Damukaradiyya da
kafirci.
7. Abubakar Shekau yace ba su san komai ba sai Littafin
Kur’ani.
8. A kan wani dalili Shugaba Buhari da sauran Musulmai
za su rika Bikin Kiresmeti wanda ba koyarwar Yesu ba ne?
9. Imani ke kara taimakon su ba kayan yaki ba.
10. Ran san a hannun Allah Madaukaki ba wani ba.
Dama
can Sojin Kasar tace an samu Littafi mai tsarki-Al Kur’ani wanda Shugaban
Kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau yake amfani da shi a Dajin Sambisa. Sojin
Kasar dai a Ranar Alhamis sun rusa kwaryar ‘Yan ta’addan na Boko Haram da ke
cikin Dajin Sambisa.
[Daga NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment