Friday, December 30, 2016

Abubuwa 10 da Shekau ya fada cikin sabon bidiyo



– Yayin da Sambisa ta fadi daga hannun ‘Yan Boko Haram sai ga Abubakar Shekau ya bayyana


– Abubakar Shekau yace Rundunar Sojin Najeriya karya take yi


– Shekau yace ba dai mutum ba sai Ubangiji






A jiya ne aka sanu wani sabon Bidiyo na Abubakar Shekau na Boko Haram inda yake karyata maganar Sojin Najeriya na cewa an fatattake su watau Boko Haram daga Sambisa. Shekau ya bayyana abubuwa da dama a sakon na sa, kamar haka:

1.      Karyar banza ce ace an fatattaki ‘Yan Boko Haram.
2.      Ubangiji ne kadai ke da iko a kan su ba Sojin Najeriya ba.
3.      Shekau yace karfi ba a bakin Bindiga ta ke ba, sai dai mai Duka.
4.      Maganar cewa an kama ‘Yan Boko Haram har fiye da 1200 karyar banza ce.
5.      Shekau ya gargadi Kasashen Duniya irin su Jamus, Faransa, Italiya da sauran su.
6.      Shekau ya kara sukar tsarin Damukaradiyya da kafirci.
7.      Abubakar Shekau yace ba su san komai ba sai Littafin Kur’ani.
8.      A kan wani dalili Shugaba Buhari da sauran Musulmai za su rika Bikin Kiresmeti wanda ba koyarwar Yesu ba ne?
9.      Imani ke kara taimakon su ba kayan yaki ba.
10.  Ran san a hannun Allah Madaukaki ba wani ba.

Dama can Sojin Kasar tace an samu Littafi mai tsarki-Al Kur’ani wanda Shugaban Kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau yake amfani da shi a Dajin Sambisa. Sojin Kasar dai a Ranar Alhamis sun rusa kwaryar ‘Yan ta’addan na Boko Haram da ke cikin Dajin Sambisa.


[Daga NAIJ Hausa]


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...