Wednesday, December 21, 2016

Gwamna Ayade zai diba masu basa shawara sama da 6, 000

 

Gwamnan Jihar Cross River ya bayyana dalilin sa na daukar mashawarta sama da 6, 000

 


Gwamnan yace yana kokarin rage rashin aikin yi ne a Jihar

 


Ben Ayade ya raba kudi ga Kungiyoyin Addini na Jihar Cross River

 

 

Gwamnan Jihar Cross-River, Ben Ayade ya bayyana dalilin da ya sa yake neman daukan Ma’aikata 50, 000 a shekara mai zuwa. An rahoto kuma Gwamnan yana kokari nada masu basa shawara guda 6, 000 a Jihar. 
 
Gwamnan yace zai yi haka ne domin Gwamnati ta rika yi da kowa. Gwamna Ayade yace idan har aka yi haka, kowane Gida zai samu jin danshin Gwamnatin Jihar. Gwamnan ya bayyana haka ne a Filin wasa na U.J Esuene da ke Jihar.

Gwamnan ya samu nasara ne dai a Kotun Kolin Kasar bayan an kalubalance nasarar da ya samu a zaben a Kotu. Kwanaki PDP ta nemi Kotun Koli ta tsige Gwamnan na Jihar Cross River daga kujerar sa, duk da cewa kuwa Gwamnan dan Jam’iyyar PDP din ne. PDP tace Gwamnan yayi karyar shekarun sa lokacin neman zabe.

Gwamnan ya kuma raba kyautar Naira Miliyan 30 ga Kungiyar Musulmai da kuma Naira Miliyan 50 ga Kungiyar Kirista ta CAN. Gwamnan yace sai ya tabbatar babu wanda ya kwana da yunwa a Jihar don haka zai dauki wadannan uban ma’aikata badi. 


Karanta shafin NAIJ Hausa domin samun cikakkun labarai


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...