Wednesday, December 28, 2016

EFCC: Gwamna zai maido abin da ya wawura



– Tsohon Gwamnan Jihar Gombe, Danjuma Goje na shirin maido wasu makudan kudi ga Hukumar EFCC


– Gwamnan da Sanata ne a yanzu yana neman a sasanta da Hukumar EFCC


– Sai dai Hukumar tace fa sai an  yi aman abin da aka ci




Tsohon Gwamnan Jihar Gombe kuma Sanata a yanzu, Alhaji Danjuma Goje zai maido akalla Naira Miliyan 40 daga cikin kudin da ake zargin ya yi awon gaba da su. Sanata Goje da wasu Mutane hudu suna hannun EFCC bisa zargin sama da wasu kudi har Naira Biliayan 25.

Cikin wadanda ake zargi akwai wanda ya kasance mai kai abinci Gidan Gwamnati a lokacin Goje yana Gwamna; Alhaji Sabo Muhammad Tumu. Akwai Alhaji Aliyu El-Nafaty da wani Dan Kasuwa; M. Dokoto.

Ana dai zargin Tsohon Gwamnan da karkatar da wasu kudin kwangila da na ‘Yan Majalisu. An dai dauki shekaru fiye da biyar ana shari’ar. Jaridar The Nation tace Hukumar EFCC na neman Tsohon Gwamnan yayi aman kudin, sai dais hi yana rokon alfarma, ayi ta-ta kare a wajen Kotu.

Kwanan nan kuma ana ta samun wasu bayanai masu cin-karo da juna a game da Majalisar Dattawar da kuma Ibrahim Magu na EFCC. Daya daga cikin Sanatocin Kasar yace ba gaskiya bane ace Majalisar ba ta amince da Ibrahim Magu ba a matsayin Shugaban Hukumar EFCC. Ana dai zargi akwai wasu da ke kokarin ganin bayan Magu na EFCC din.





No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...