Monday, December 19, 2016

Boko Haram: Shin ina Musuluncin Shekau?

– Sunan Abubakar Shekau ya samu shiga cikin Manyan Musulman Duniya

 


– An kuma saka sunan Shugaba Buhari da Sultan, Abubakar Sa’ad

 


– Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya sha cewa ‘Yan Boko Haram din ba musulunci suke yi ba

 

 

Wata Jarida ta lissafo sunayen Musulman da suka yi kaurin-suna a Duniya, a ciki har da su Shugaban Kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau. Sauran wadanda suke cikin jerin sun hada da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da kuma Sarkin Musulmi, da irin su Hamshakin Dan Kasuwan nan, Aliko Dangote. 

Ko a shekarar bara an saka sunan Shugaba Buhari a matsayin Musulman da suka yi fice a Duniya. Jaridar ta kuma bayyana cewa Musulmai sun kusa kai kashi daya cikin hudu na mutanen Duniya; akwai Musulmai kusan biliyan biyu. 

Shugaba Buhari ne na 17 a jeringiyar sunayen Mutane 500 din da aka jero. Ciki kuma akwai Sarkin Musulmi; Abubakar Sa’ad III. Akwai kuma Babban dan kasuwan nan Alhaji Aliko Dangote da ma kuma Babban malamin nan Shehi Ibraheem Saleh. 

Sannan dai an saka sunan Abubakar Shekau a ciki Musulmai 500 da suka yi fice. Sai dai wasu na ganin bai dace a ambaci Shekau din cikin wannan sahu ba. Boko Haram dai ta kashe mutane fiye da 30,000 karkashin shugabancin Abubakar Shekau. Ya kasance yana amfani da kananan yara mata wajen tada bam da sunan Addinin Musulunci wanda har ISIS sai da ta gargade sa.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...