Friday, December 16, 2016

An kama Gwamna kuru-kuru a waya yana neman murde zabe





Asirin Gwamna Wike ya tonu

 

An kama Gwamnan Rivers, Nyesom Wike a wayar tarho yana kokarin murde zabe

 



An ji cewa Gwamnan ya biya Ma’aikatan Hukumar zabe kudi domin su yi murdiya

 



Gwamnan yace zai kashe Ma’aikatan INEC din idan ba su yi yarda yake so ba

 

 Ku maido mani kudi na ko in kashe ku… Aka ji Wike yana fadawa Ma'aikatan INEC a tarho


An samu muryar wayar tarho da Gwamnan Jihar Rivers yayi da Jami’in Hukumar zabe na INEC. An ji Gwamnan da kan sa yana shan alwashin kashe daya daga cikin Jami’an zaben da aka turo Jihar daga Plateau. 

Sahara Reporters ce dai ta fito da wannan sako. An ji cewa Gwamnan yayi alkawarin kashe wani Jami’i da ya gagara. Da alamu Jami’in Hukumar zaben ya ki amincewa da ya saka hannu a takardun zaben ne. Gwamna Wike yace zai kashe kowane ne.

A cikin wayar an ji Gwamnan yana fada da Turanci cewa ‘zan tabbatar na kashe shi… zan ga bayan sa a Jihar nan. Ba matsala.’ Gwamnan yake cewa: ‘Ka kira wannan wanda aka turo daga Plateau, ya gargadi mutanen sa da ke Khana… duk abin da muka basa… Idan ba haka ba, ba zai bar Jihar nan lafiya ba'

Dama dai Jam’iyyar APC tace Gwamna Wike yayi tafka magudi a zaben da ya gudana makon da ya gabata.

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...