Dan Majalisan da aka kora ‘Jibrin’ ya karyata
rade-raden sulhu
– Tsohon Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na
Majalisar Tarayya, Abdul Jibrin ya bayyana cewa har yanzu yana kan bakan sa
– Jiya an rahoto cewa ya
shirya zama domin ayi sulhu da Shugaba Yakubu Dogara
– Hon. Jibrin yace wannan karyar banza ce,
asali ma yanzu ya fara
A jiya
da rana ne Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa Tsohon Shugaban Kwamitin Kasafin
Kudi na Majalisar, Hon. Abdulmumuni Jibrin wanda ke wakiltar mazabar
Kiru/Bebeji na Jihar Kano ya shirya yin sulhu da Shugaban Majalisar, Yakubu
Dogara.
A jerin
wasu sakonni da Dan Majalisar ya aika ta shafin Twitter, ya bayyana cewa wasu
daga cikn yaran Shugaban Majalisar, Yakubu Dogara ne da wannan danyen aiki.
Jibrin yace Turaki Hassan ne ya yada wannan rade-radin na karya. Yace yana nan kan bakan sa, babu gudu-ba ja
da baya.
Honarabul
Jibrin yace babu wani sasantawa da yake kokarin yi da Kakakin Majalisar; Yakubu
Dogara ko ta wasu ‘Yan Majalisar ko Dattawan Kasar kamar yadda ake rade-radi.
Yace nan gaba kadan ma zai tona wasu asirin.
Majalisar
Wakilai ta Tarayya ta tsige Tsohon Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar,
Abdulmumuni Jibrin bayan da ya zargi Shugaban Majalisar wakilan Kasar, Dogara
Yakubu da wasun su da laifin handame wasu kudi daga kasafin bana.
No comments:
Post a Comment