Wednesday, December 14, 2016

Nnamdi Kanu zai yi aman wuta





– Nnamdi Kanu yace idan ya bude baki yayi magana sai Najeriya ta wargaje

 



Ana nan ana ta shari’ar Nnamdi Kanu

 



Kotu tace ba za ta sake Kanu ba, don kuwa laifin sa ba na wasa bane

 



Wata sabuwa: Shugaban Kungiyar ‘Indigenous People of Biafra’ Watau (IPOB) ta Biafra Nnamdi Kanu, yace zai rikita Najeriya kuma mai gidan Rediyon Biafra yace idan har yayi magana fa Kasar nan za ta watse. 

Ana nan dai ana ta shari’ar Nnamdi Kanu, wanda yake rike tun bara. Kotu tace ba zai yiwu hakanan ta bada belin Kanu ba don kuwa akwai abin ba na wasa bane. Alkali mai shari’a Nyako tace ba za ta saki Nnamdi Kanu da sauran wadanda ake kara ba. Nnamdi Kanu yace kokari ake yi a ga bayan sa, kamar yadda aka kashe mutanen su a Kasar Ibo. 

Babban Kotun Tarayya da ke Abuja tace za ta bada damar a fara bada shaida kan karar amma ba tare da an ga masu bada shaidar ba. Sai dai Kanu da Lauyoyin sa sun ce ba za si yarda da wannan ba ko kadan. 

Kanu yace da Kotu Buhari na kokarin ganin bayan sa ne kurum. Har sai da ta kai Lauyan na sa, Lauya Chucks Mouma SAN ya roke sa da yayi shiru a Kotun. Kanu yace idan ya bude baki Najeriya za ta tashi.

[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...