Saturday, December 10, 2016

Hudubar Jumu’a daga Masallacin I.T.N

NEMAN HALAL A DUNIYA DOMIN LAHIRA

 

Hudubar Jumu’a daga Masallacin I.T.N Zangon-Shanu, Zaria


 

Daga Bakin Sheikh Salihu S. Abubakar

 

 

BismilLahir Rahmanir Rahim.

Dukkan Godiya ta tabbata ga Allah, Shine wanda ya kammala mana addinin mu, kuma ya cika mana ni’momi. Muna godiya da yabo gare Shi Madaukakin Sarki, Shine yayi mana wata babbar baiwa ta hanyar aiko da Mafificin ta’likai duka-Shugaban mu, Annabi Muhammad SAW. Muna shaidawa cewa lallai babu abin bautawa da gaskiya face Allah, shi kadai ya ke, ba shi da abokin tarayya. Shi kuma Allah, yayi alkawari ga masu tsoron sa cewa zai saka su cikin Gidan Aljanna-Gida na Aminci. Muna shaidawa lallai Shugaban mu, Annabi Muhammad SAW Bawan Allah ne, kuma Manzon sa, wanda yake mai Madaukakin daraja da kuma mafi daukaka na mukami.
Bayan haka:
Ya ku ‘Yan uwa, lallai Allah SWT, tsarki ya tabbata gare sa tare da daukaka, ya fadi a cikin Littafin sa mai girma. Allah SWT yace: ‘Lallai, Hakika, A gare ku akwai kyakkawan abin koyi a cikin tafarkin Annabi Muhammad SAW, ga duk wanda yake fatan samun yardar Rahamar Allah da kuma Ranar Lahira...’ Saboda haka, babu makawa gare mu, lallai ne mu yi duk abin da za mu iya saboda mu yi koyi da irin halayen sa da dabi’un Sa, Shi Manzon Allah SAW. Shi ne abin koyi, Shi ne jagora da ya kamata mu bi. Kuma babu lokacin da muka fi bukata muyi koyi, kuma mu siffantu da dabi’un sa kamar wannan lokaci da muke ciki. Shi SAW ne ya karantar da mu abin da wannan Duniya ta ke ciki gaba daya. Shi SAW ne ya fada mana cewa Duniyar nan Halittar Allah ce, kuma Allah ya kawo mu wannan Duniya domin jarrabawa, kuma za mu koma gare sa. Shi SAW ne ya mana bayanin menene manufa a cikin wannan rayuwa ta duniya, Shi ne yayi mana bayanin tafarkin da ya kamata mu bi a cikin rayuwar mu ta Duniya. Saboda haka, duk wanda yayi koyi da irin shiriyar Sa ya rabota, ya kuma yi nasara. Wanda kuma ya aikata sabanin haka, ya bata, kuma ya halaka. 
Shi Annabin mu, SAW ya karantar da mu cewa ita rayuwar Duniya tana da Manufofi wadanda suke guda 2. Manufar farko ita ce Bautar Allah, sannan manufa ta biyu ita ce mu rayar da wannan samuwa watau mu raya wannan Duniya baki daya. Ko da yake wannan manufa ta biyu, bangare ne na wancan na farko. Ma’ana; aikin da za muyi wajen raya duniya, duk wani bangare ne na Aikin Bautar da Allah SWT ya wajabta mana. Allah ya fada cikin Al-Kurani cewa: ‘Ban halicci mutane da Aljani ba, sai don su bauta mani’. Kuma shi Allah Madaukaki SWT ne yace; shi ne wanda ya tsirar da halittar ku daga cikin Kasa, kuma ya sa ku raya ta. Watau ku za ku raya ta, ku gyara ta, ita Duniya.
Allah SWT ya umarci Dan Adam yayi riko da sababi a cikin rayuwa, wanda za su zama daukaka ga Al’ummar mu da kuma gyara rayuwar mu ta duniya domin ta zama matakala zuwa Lahira.  Kuma wannan Addinin na mu kamar yadda Manzon mu Annabi Muhammad SAW ya karantar da mu, ya hana mu shantakewa da lalaci da ragwanci. Saboda ba zai yiwu ba a cin ma abin da Allah yake so a ban Kasa da lalaci da kuma ragwanci. Allah Madaukakin Sarki ya fada mana cewa: ‘Shi Allah ne wanda ya sanya Kasa ta zama horarriya, saboda haka, kuyi ta yawatawa cikin sasannin ta, kuma ku ci daga cikin arzikin Allah, kuma gare sa za ku taru.’
Saboda haka Musulunci ya karantar da duk abin da ake bukata wajen rayar da Duniya, ta wannan hanyar ne kuma za a samu gina lahira. Musulunci ya kuwa kwadaitar da cewa a yawata a cikin Kasa, a zurfafa cikin sasannin Kasar wajen samun arziki mai albarka wanda yake cikin tudu da kuma ruwa. Tare da kuma karfafa gwiwa da Musulunci yayi a kan a tashi ayi aiki tukuru, ya zo a cikin Hadisin da Miqdam ya ruwaito cewa: Annabi SAW yace: ‘Babu wani abinci da daya daga cikin ku zai ci, da ya fi abin da mutum ya aikata da hannun sa, ya samo...’ Sai Annabi SAW ya cika da cewa kuma Lallai Annabi Dawud AS, ya kasance yana ci ne daga aikin hannun sa. 
[Imamul Bukhari ya kawo wannan Hadisi.]
Saboda haka shi Musulunci, wanda Manzon Allah SAW ya zo mana da shi, kira ne baro-baro da cewa duk wanda ya yarda da Musulunci ya tashi yayi aiki tukuru domin tabbatar da Duniya da raya ta, ta yadda za a jawo Alheri ga dukkan Duniya. Shi Musulunci ya girmama al’amarin aiki tukuru, ya kuma sa hakan ya zama hanya da zai kai mutane ga cigaba da daukaka a nan duniya, kuma ya zama ibada.
Ayoyin Qur’ani sun kwadaitar da karfafa gwiwa wajen tashi da yin aiki tukuru a wajen al’amarin rayuwa da kuma abin da zai kawo abinci da tufafi da sauran bukatu na mutum da iyalan sa. Saboda haka ne Allah SWT yayi umarni da Sallar Jumu’a, bayan Sallar kuma yayi umarnin a bazu cikin Kasa domin a nema daga cikin falalar Allah. Allah Madaukakin Sarki yace: ‘Idan an gama Sallar Jumu’a, ku bazu a cikin Kasa, ku nema daga cikin Rahamar Allah, amma ku rika tuna Allah ko ku samu babban rabo.’ Wannan umarni ne Allah, kamar yadda aka yi umarni da azo Masallaci ayi Sallar Jumu’a, haka aka yi umarni da a yadu a ban Kasa, a nema daga cikin falalar Allah bayan an tashi daga Masallacin.
Hakika wannan Addini na mu na Musulunci yayi mana bayani cewa duk wanda yayi ta kokari domin neman abincin sa da na ‘ya ‘yan sa ta hanyar halal, yana daidai da darajar wanda ya mutu shahidi a wajen yaki ko kuma wanda aka sa gadi ya tare kofofin da abokan gaba za su kawo hari. Saboda haka, yana daya daga cikin wadanda suka yi aiki ta hanyar daukaka kalmar Allah. Akwai Hadisi daga Ka’ab Dan Ujrah RA yace; Wani mutum ya wuce ta gaban Manzon Allah, sai Sahabbai suka ga irin kirar jikin sa da kuma kuzarin sa, wannan abu ya ba su sha’awa, sai suka ce da RasululLah SAW cewa dama ace wannan mutumi yayi amfani da kuzarin sa cikin tafarkin Allah. Sai Manzon Allah SAW yace ai in dai yana kokari ne domin nemawa kan sa da iyalin sa; kananan yara, abinci ne, to yayi cikin tafarkin Allah. Yace idan kuma ya fita ne domin samun abin da Mahaifan sa-da suka tsufa za su ci, shi ma duk cikin Tafarkin Allah ne. Manzon Allah SAW yace idan har ya fito ne domin samun abin da zai ci, ya kare kan sa daga fadawa sharri, to wannan duk cikin tafarkin Allah ne. Amma idan ya fito ne domin ya samu abin da zai yi alfahari da shi, ko ya tara arziki, to wannan yana cikin Tafarkin Shaidan. Imamul Tabarani ya fito da wannan Hadisi.
Shi kuma Musulunci bai ma tsaya ga karfafa mana gwiwa kawai ba, ya kuma neme mu da muyi aiki da kyau; babu magudi da ha’inci. Wannan shi ne abin da Manzon Allah SAW ya koyar da mu-kyautata aiki. Wannan saboda mu samu soyayyar Allah da kuma Rahamar sa. An sami Hadisi daga Aisha RA tace: Manzon Allah yace: Lallai Allah mai girma SWT yana so idan mutum zai yi wani aiki, ya tsaya yayi sa za-kyau. Allah SWT da kan sa yana fada mana cewa: Ku kyautata domin Allah yana son masu kyautatawa.
‘Yan uwa ina so ku rike wannan daga cikin Hudubar; Idan za mu rike Addinin mu da kyau, mu rika biyayya kuma mu tashi muyi aiki tukuru; don babu wani aiki na Duniya-wanda yake dabam da na Lahira, wannan ba karantawar Addinin Musulunci bane. Kowane aikin Duniya, ana yin sa ne domin neman Lahira, ko da a zahiri za mu ga cewa an ci moriya a Duniya, ana aikin ne domin Lahira. Duk wanda ya dauka cewa akwai wani aikin neman Duniya da kuma na Lahira, bai fahimci Addinin Musulunci ba. Wane lokaci ne na Allah, wane lokaci ne kuma na mutum? Duk lokacin ka na Allah SWT ne; daga kasuwanci, aikin Gwamnati, zuwa noma dsr. Duk aikin da mutum yake yi, idan har ka tsaya kayi aiki yadda Allah yace, to wannan aikin ibada ne kuma zai ba mutum matsayin shahidi, haka wannan lamari yake. Saboda haka, ya kamata kowa ya fahimci wannan, muddin muka fahimci wannan, za mu gina rayuwa mai kyau a nan Duniya da kuma Lahira.
Allah ya bamu fahimtar AlQurani mai Girma, ya amfane mu gaba daya da abin da ke cikin sa na Ayoyi masu wa’azi da hikima. Allah ya tserar da mu daga Azabar sa mai radadi. Allah kayi dadin tsira ga Annabin Ka SAW da iyalan sa kamar yadda ka yi dadin tsira ga Sahabban Manzon Allah SAW da wadanda suka bi bayan su bisa tafarki madaidaici. Allah ka kama hannuwan wadanda ka Shugabantar da su a matakai dabam-dabam zuwa ga abin da kake so ka yarda shi.



Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga Zaria.

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...