– Wani Coci ya rushe a Akwa-Ibom inda da dama suka hallaka a sanadiyar haka
– Shugaba Muhammadu Buhari ya aika ta’aziyar sa ga wadanda abin ya shafa
– Shugaban Kasan ya kira Gwamna bayan abin ya faru
Coci ya rushe a Akwa-Ibom, da dama
sun hallaka
Wani
Coci ya rushe a Akwa-Ibom, wanda hakan yayi sanadiyar rasa rayukar daruruwan
mutane. Wannan abu dai ya faru ne a Babban Birnin Akwa-Ibom, Uyo. Gwamnan
Jihar, Udo Emmanuel ya tsallake rijiya da baya shi ma.
Shugaba
Buhari ya mika ta’aziyar sa ga wadanda abin ya auka da iyalan su. Mutane fiye
da 100 ne dai suka rasa rayukan su. Jaridar Premium Times tace ginin Cocin gaba
daya ya zube Kasa war-was.
Gwamnan
Jihar yana cikin wadanda ke cikin Cocin, sai dai daf da abin zai faru ya fita.
Amma mutane da dama, ba su taki wannan sa’a ba. Rahotanni sun nuna cewa yanzu
Sakataren Gwamnatin Jihar Akwa-Ibom da kuma Sakataren yada labarai suna asibiti
kwance.
Shugaba
Buhari ta bakin Garba Shehu yace Shugaban Kasa ya kira Gwamna Emmanuel ta wayar
tarho, inda ya masa murnar tsira da rayuwar sa, ya kuma jajanta masa abin da ya
faru a Jihar sa.
No comments:
Post a Comment