– Tsohon Shugaban Kasa
Goodluck Jonathan ya kawar da kura game da batun tsayawan sa takara mai zuwa
– Ana ta yada cewa Tsohon Shugaban
na shirin kara dawowa
– Goodluck Jonathan yace duk zancen banza ne na mutane
Tsohon Shugaban Najeriya,
Dr. Goodluck Jonathan ya musanya labaran da ke yawo na cewa zai kara tsayawa
takarar Shugabancin Kasar nan. Jaridar The Nation ta rahoto Shugaban yana
karyata jita-jitan da ake ji.
Shugaba Jonathan yayi jawabi
ne ta kafafen yada labarai inda ya kira labaran da sunan kirkirar mutane. A
baya an ce Jonathan ya gana da mutanen sa domin ganin yadda zai dawo mulki.
Yace karya ne don a lokacin ma ba ya gida, sai kwanan nan ya dawo domin kiresmeti.
Tsohon Shugaba Jonathan
Goodluck dai yayi abin da ba a taba yi ba a Kasar nan. A zaben Kasar da ya wuce
Shugaban ya sha kashi lokacin yana kan mulki a hannun Jam’iyyar adawa.
Salin-alin Shugaban ya tattara ya bar mulkin ba tare da wani jayayya ba.
Tsohon Shugaban Kasar ya sha
fada cewa bai dace a zubar da jinin ko mutum daya ba a Kasar saboda manufar sa
shi daya, don haka ne ya sauka daga mulki. Jonathan di yayi wa masu bikin
Kiresmeti fatan alheri.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment