Monday, December 26, 2016

Ka ji abin da cin hanci ya jawowa wani Dan Sanda


Jami’in Dan Sanda yayi fada da Direban mota...ya rasa Bindiga


– An ga wani Dan Sanda yana fada da Direba a Legas


– Jami’in ya rasa Bindigar sa wajen kokarin karbar N500


Wannan abu ya faru ne a Ikorodu ta Legas

An ga wani Dan Sanda yana fada da wasu mutane uku a Unguwar Ikorodu ta Jihar Legas. An dauki hoton wannan Jami’i ne yayin da rikici ya rincabe tsakanin sa da wani Direban mota a wurin.

A dalilin haka ne ma Dan Sandan ya rasa Bindigar sa wajen kokawa da mutanen. An ji wani daga ciki yana kiran a dauki Dan Sandan hoto, don kuwa ta shi ta kare idan aka yi haka. Hakan dai kuwa aka yi.

Saboda dai cin hancin N500 ta kai wannan Dan Sanda ya rasa bindigar sa. Kamar yadda The Punch ta bada labarin bidiyon da aka yada. An ga Dan Sandan yana kokarin karbar cin hancinn N500 daga hannun Direban wata babbar mota. 

A Garin Zariya kuma, Jiya da safe, an samu takaddama tsakanin Soja da wani Jami’in tsaron, har ta kai wannan Jami’in nan Mobile Police ya shiga buda wuta babu dalili a gaban wani Bankin Zenith da ke Unguwar PZ.








No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...