Ka ji sirrin Gwamnatin Buhari na
Yakar sata a Kasa
– Gwamnatin Shugaba Buhari na bi a
hankali wajen yaki da rashawa a Kasar
– Ministan watsa labarai na Kasar
ya bayyana haka
– Alhaji Lai Muhammad yace wasu
suna kokarin nuna ba haka lamarin yake ba
Ministan
watsa labarai da al’adu na Kasar nan, Alhaji Lai Muhammad, ya bayyana cewa
Gwamnatin Shugaba Buhari na bi a hankali wajen fada da cin hanci da rashawa a
Najeriya. Ministan ne dai ya bayyana haka da kan sa a Yau da yake Legas.
Hakan
na zuwa ne bayan da Lai Muhammad din yace an kama wani Babban Jami’in Gwamnati da yayi awon gaba da
manyan motoci kirar SUV har guda 40. Wani Sakataren din-din-din ya kasa-ya
rabawa kan sa wadannan motoci shi kadai ba tare da ko Bismillah ba.
Lai
Muhammad ya bayyana irin matakan da Gwamnatin Kasar ta ke bi domin hana cin
hanci da rashawa. Lai Muhammad yace an kawo tsarin nan na asusun bai daya watau
TSA, sannan kuma an nada Kwamiti da dama domin su tattara abin da Gwamnati ta
karbo daga hannun barayin Kasar.
Kwanan
nan ne ma dai Gwamnatin ta kawo wani tsari na tona asiri-ka-samu-kason ka.
Sannan kuma an gano ma’aikatan bogi da dama wanda albashin sun a shekara ya kai
Naira Biliyan 200.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment