Tuesday, December 20, 2016

Shia: Gwamnati ta haramta tattaki

– Gwamnatin Jihar Kaduna ta haramta tattaki a fadin Jihar

 


– Gwamnati tace daga yanzu babu wani taro na gaira-babu dalili

 


Ana hakan ne domin a kawo karshen ‘Yan kungiyar IMN na Shi’a a Jihar

 


Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana cewa daga yanzu babu wani tattaki ko gangamin da ya sabawa doka a Jihar. Gwamnatin tayi wannan ne domin kawo karshen lamarin ‘Yan  Kungiyar IMN na Shi’a a Yankin. 

Mai magana da bakin Gwamnan Jihar Nasir El-Rufai, Samuel Aruwan ne ya tabbatar da haka a wani jawabi da ya fitar a jiya. Bayan wani taro da Jami’an tsaro na Jihar, Gwamnan ya dauki wannan mataki na dakatar da ‘Yan Kungiyar har tsawon wani lokaci.

Kafin yau dama can Hukumar ‘Yan Sanda sun gargadi ‘Yan Kungiyar. Bayan nan ne Gwamnati ta saka Kungiyar cikin ‘Yan tawaye, wanda Kungiyar tace ba za ta yarda ba. 

Gwamnan yace anyi hakan ne domin kawo zaman lafiya a Jihar. Gwamnan yace zai Hukunta duk wanda ya saba wannan doka.


[NAIJ Hausa]



No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...