Sunday, December 4, 2016

Wani Dalibi daga Najeriya ya ciri tuta a Ingila

Wani Dan Arewa ya taka rawar gani

Wani dalibi daga Arewa ta Najeriya ya taka rawar gani a Kasar Ingila

 


Marzuq Ungogo ya gama da mataki na farko a karatun digirin san a biyu

 


– Haziki Marzuq Ungogo ya kammala digirgir a Jami’ar Glasgow

 

 

Wani dalibi dan Arewa ya ciri tuta a can nesa Kasar Ingila. Marzuq Ungogo ya gama da matakin farko wajen karatun Digirin sa a Jami’ar Glasgow ta Kasar Birtaniya.

Marzuq mutumin Kasar Kano ne, kuma yayi Digirin sa a Jami’ar nan ta Ahmadu Bello ta Zariya, inda ya karanta Ilmin likitan dabbobi. Ko a Digirin na sa na farko dai, Marzuq ya ciri tuta a Jami’ar, inda ya ko kammala da matakin farko watau ‘first class’ a shekarar 2014.

Wannan haziki ya samu shaidar karantar Ilmin da ke lura da yadda magunguna ke aiki a jikin halittu watau ‘Clinical Pharmacology’ a Jami’ar Glasgow da ke Kasar Birtaniya. 

Kwanaki ma dai an samu wani gwarzo dan Arewa mai suna Adamu Tilde da ya taka rawar gani a wata Jami’ar Kasar Hungary. Shi ma Tilde, ya kware ne a fannin ilmin dabbobi. 

Allah ya kara mana irin su.

1 comment:

  1. Khalid Garba MohammedDecember 4, 2016 at 4:46 PM

    Muna matukar alfahari da wannan dalibi kuma abokin mu Marzouq. Allah ya kara masa hazaqa.

    ReplyDelete

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...