Saturday, December 17, 2016

Hudubar Juma’a daga mimbarin ITN-Zaria



‘Riko da Sunnar Ma’aiki SAW’-Daga Bakin Imam Ustaz Sa’eed Yunus.


Assalamu Alaikum wa Rahmatul Lah, 

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah SWT wanda ya cika mana addinin mu. Babu wanda ya isa ya kara wani abu a cikin Addini face yana da wata hujja daga Allah ko daga Manzon Allah SAW. Ina gode masa, ina tuba gare sa, ina neman gafarar sa, ina shaidawa cewa shi kadai yake ba shi da wani abokin tarayya. Shi ne ya shar’anta mana Addini ya sawwaka shi, ya hukunta al’amari. Allah SWT shine wanda yayi mana ni’ima wanda ba su kirguwa. 

Ina shaida cewa Annabin Mu, Annabi Muhammadu SAW, Bawan Allah ne kuma Manzon Sa. Shi ne wanda yayi bushara da Al’umma, kuma Shi mutum ne tamkar sauran mutane wanda Allah SWT ya aika Shi ya kasance rahama ga Duniya gaba daya. Allah SWT ya aiko Annabi Muhammadu SAW domin ayi da’a gare sa kuma ayi biyayya, ba don a saba masa ba; ba don ayi kari cikin Addini ba, ba don ayi kirkira ba. Babu Imanin da zai inganta face an yi da’a ga Manzon Allah SAW wajen aiki. A cikin lamura, duk wanda yake so ya ci nasara, ya bi Ma’aiki SallaLahu Alaihi Wasallam. ‘Yan uwa, ku sani cewa nisantar abubuwa na kirkire-kirkire a rayuwa, abu ne da ke sa a ci nasara a rayuwa. Tsira da amincin Allah su tabbata ga wannan farin jakada na Allah, Annabi Muhammadu SAW.Mu ji tsoron Allah, mu sani cewa Allah ya aiko mana Manzo daga cikin mu. Tsayuwa a kan abin da Annabi SAW ya zo da shi da shari’ar Manzon Allah, cin nasara ce. Haka nisanta da kuma abin da mutane suka kirkira, wannan nasara ce.

‘Yan uwa mu sani fa ita Bidi’a, ita ce abin da Allah SWT bai saukar da wani dalili a kan sa ba. Lallai Manzon mu Annabi Muhammad SAW yayi umarni da a rike Sunnah ta sa. Manzon Allah SAW yayi wannan umarnin sau da yawa; kuma wannan umarni ya tabbata cikin Al-Kur’ani mai girma; haka ma kuma Hadisai sun tabbatar da abin da wadannan ayoyi suka fada game da sabawa Ma’aiki. A ji tsoron sabawa Ma’aiki, gudun musiba ta samu mutum ko wajen mutuwa, ko a Ranar Lahira a ce da shi ba ka cikin wadanda suka bi koyarwar Ma’aiki. Annabin Rahama SAW yana cewa a wani Hadisi da Imamu Ahmad da Abu Dawuda da Tirmidhi da Ibn Majah suka fitar da shi daga Irbab dan Sariya RA yake cewa: Manzon Allah SAW yace: Duk wanda ya rayu daga cikin ku, zai ga sabani mai yawa. Saboda haka, ina kiran ku, ku rike Sunnah ta, da Sunnar Magabata shiryayyu, ku rike ta, riko mai karfi da turaman hakora…Sannan Annabi SAW yake cewa: Ina yi maku kashedi da abin da aka kirkira, lallai duk abin da aka kirkire sa, fararre ne, kuma dukkan wani abu shi ake cewa Bidi’a, kuma Bidi’a bata ce, kuma bata tana cikin wuta. Allah ka kare mu. 

Abdullahi Dan Abbas RA, yana cewa: Babu wani zamani da zai zo wa mutane, face sun kirkiro wani abu na Bidi’a, kuma su zo su rufe Sunnar Manzon Allah. Su kife Sunnah, su kuma rayar da Bidi’a. Dan Abbas yace wannan zai jawo masu bala’i. Abdullahi Dan Umar RAA yana cewa: Dukkan wata Bidi’a bata ce, ko da mutane suna kallon ta mai kyau. Imam Al-Lalaka’i ya fitar da wannan a cikin Littafin Sharh Usulul I’tiqad Ahlul-Sunnah wal Jama’a. Imamuna Malik yana fada cewa: Babu abin da zai daidaita wannan al’ummar ta karshe, face abin da ya gyara al’umma ta farko. 

‘Yan uwa masu girma kun ji abin da manyan Magabata, Bayin Allah suke fada game da Addini. Wani daga cikin Magabata yana cewa: Dukkan wasu hanyoyi wadanda za a bi domin a gane Addini, an riga an rufe su, face abin da ya dace da karantarwar Annabi Muhammadu SAW. Imam Ibraheem Al-Nakha’iy Allah ya masa Rahama yana cewa: Duk wanda ya kirkiri wani abu daga cikin abubuwa na Addini, wadanda ba su cikin Addini, yana masa kallon abu ne mai kyau, kamar yana tuhumar Manzon Allah SAW ne da cewa yayi ha’inci game da risala watau sakon Annabta. Ibraheem Al-Nakha’iy yake cewa Allah ya fada Lallai Annabi SAW ya cika Addini.
Allah ka azurta mu bin hanya madaidaiciya, da koyi da Shugaban mu Annabi Muhammadu SAW. Allah ka nisantar da mu da bin Bidi’a. 

Bangare na biyu na Huduba.

Bayan Godiya ga Allah wanda yayi umarni da biyayya gare sa da kuma Manzon sa, Annabi SAW; wanda yayi hani game da kirkirar Bidi’a. Ina shaidawa ba sa da Abokin Tarayya, kuma ina shaidawa Annabi Muhammadu SAW Bawan Allah ne, Manzon Sa. 

‘Yan uwa masu girma mu sani cewa ita gaskiya ana sanin ta ne ta hanyar dalili. Ana gane gaskiya ne da dalili na shari’a ba da yawan aikin Mutane ba. Ka da ka rudu da yawan masu kirkirar Bidi’a; abubuwan da ba su tabbata ba cikin Addini. Allah yayi kashedi cewa: Idan ka bi yawan mutane a ban Kasa, za su hallakar da kai. Yawa ba shi bane abin lura, A’a, Ina dalili? 

Ina mana wa’azi game da abubuwa da suke aukuwa lokaci bayan lokaci, wasu mutane suna kirkirar abubuwa suce Addini ne, Amma babu karantarwa a cikin Addini game da shi. Sai ka ji cewa kawai, mun ga mutane suna yi ne kurum. Allah ya fada cewa wasu suna fadan: Mun ga Iyayen mu ne kurum suna aikatawaWannan ba dalili bane, sai dai abin da ya tabbata a Sunnah. 

Mutanen da suke kokarin raya Bidi’a, Makaryata ne kurum, suna nema su gusar da sha’awar su da yunwar da suke ji; su dai su ci, su more. Daga nan kuma kawai sai a fara kirkirar wargi da wasa da karya. Wadanda suke kira ga wannan al’amari suna kokarin nunawa al’umma cewa Annabi bai isar da sako ba, suna kokarin kawo shakka ga Sunnar Manzon Allah. ‘Yan uwa ku fadawa duk wanda yake kirkirar abin da Annabi SAW bai yi ba cewa wannan abu yana dawo da mu baya. 

‘Yan uwa masu girma, Huduba tana fada mana cewa yaushe ne mutane za su farka daga wannan bala’i? Ina Addini da kishi na Tauhidi? Ina riko da Kur’ani da son Manzon Allah SAW da ake takama da shi? Lallai Annabi SAW ya fada mana cewa Musulunci ya zo bako, kuma zai koma bako. Yau ga bakon Addini muna gani, Mutane suna ta kirkirar abin da Annabi SAW bai yi ba. Ya ku ‘Yan uwa Musulmi, ya ku masu son Manzon Allah, ku rike Sunnar Manzon Allah, ku kiyayi kirkirar abubuwa a cikin Addini. Ayi riko da Sunnah kamar yadda Annabi ya koyar; za a ci nasara, kuma za a samu babban rabo. Lallai mutane su sani cewa dukkan Bidi’a sharri ce, Lallai dukkan Bidi’a da aka danganta ta da Addini, sharri ce. Domin ita Bidi’a tana cikin Addini ne, abin da ya shafi mu’umala ba a kiran sa Bidi’a. Wanda ya kirkiri wani abu wanda ba ya cikin Addini, ya kuma ce Manzon Allah SAW ne ya fada, to za a maida masa, kamar yadda Hadisai suka nuna.

‘Yan uwa ba ku ga abin da yake faruwa na rafkana da magagi ba ga Mutane? Wallahi daga cikin wadannan abubuwan da suke aukuwa aka rasa gane bakin zaren, har da Bidi’ar da mutane suka dangana ga Manzon Allah SAW. 

Muna rokon Allah ka sa mu kiyayi abin da Manzon ka ya hana mu aikatawa. Kuma Allah ka sa mu cikin wadanda ba su alfahari. Wannan Huduba tana nunawa mutane cewa su dawo cikin hankalin su.
Allah ka azurta mu da kyakkayawar biyayya ga farin Jakadan ka, Annabi Muhammad SAW. Allah ka buwaiyar da Addinin Musulunci da Musulmai ka kaskantar da Kafirci da Kafirai. Allah ka biya mana bukatan mu…
Ameen.


Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga Masallacin I.T.N-Zaria.
Muhammadmalumfashi@gmail.com          
Twitter:@Ya_waliyyi

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...