Monday, December 12, 2016

Majalisar Dinkin Duniya za ta dauke Ministar Buhari

Daya daga cikin Ministocin Buhari ta samu babban matsayi a Majalisar Dinkin Duniya

 


UN za ta nada Amina J. Mohammed a matsayin Mataimakiyar Shugaba

 


– Ministar tayi aiki da Shugaban Majalisar Dinkin Duniyar

 

Shugaba Buhari zai rasa Minista

Da alamu Majalisar Dinkin Duniya za ta dauke daya daga cikin Ministocin Najeriya. Amina J. Mohammed tana dai cikin Ministocin da suka fi kowa kokari a Gwamnatin Shugaba Buhari. Yanzu haka labarai na zuwa cewa Majalisar Dinkin Duniya za ta ba ta babban matsayi. 

Jaridar Premium Times tace an gama shirin nada Amina Mohammed a matsayin Mataimakiyar Shugabar Majalisar Dinkin Duniya, kuma nan da wani dan lokaci za a sanar. Sai dai Fadar Shugaban Kasa tace ba ta san wannan ba, Shugaban Kasa yace har yanzu Amina Mohammed, Ministan Kasar ce.
 
Ministan tana ta kokari wajen ganin an tsabtace muhallin Kasar. Kwanaki Gwamnati ta kaddamar da shirin Ogoni na Neja-Delta, inda Man fetur ya gurbata. 

Amina Mohammed tayi aiki da Shugaban Majalisar Dinkin Duniya, Ban-Ki Mon kafin nan. Zuwa Junairun badi ne dai za a sake sababbin Shugabannin Majalisar ta Dinkin Duniya watau UN. Kwanakin baya dai Shugaba Buhari ya rasa wani Ministan, har yanzu kuma ba a maye gurbin sa ba.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...