– Shugaban Kasar Gambia yayi tir Kungiyar ECOWAS ta Afrika
– An nada Shugaban Kasa Muhammadu Buhari wanda zai sasanta rikicin siyasar Kasar Gambia
– Sai dai Yahaya Jammeh yace wannan duk ba za su sa ya janye ba
Kasar Gambia: Shugaba ba zai sauka ba
Shugaban Kasar Gambia ya sanar a Gidan Talabiji cewa ba
abin da zai sa ya sauka daga Shugabancin Kasar. Karshen makon can ne Shugaba Buhari
da wasu Shugabannin Afrika su ka kai ziyara Kasar domin ganin Shugaba Jammeh ya amince da
sakamakon zaben da ya sha kashi.
Shugaba Yahaya Jammeh yace dai ziyarar da su Buhari suka
kai bai canza komai ba. Yace babu dalilin da zai sa ya sauka daga mulkin Kasar.
Shugaban Kasar ya sanar a Talabijin cewa kawai bata lokaci ne su Buhari suke yi
don kuwa yana nan daram-dam a kujerar mulki.
Jaridar This Day ta kawo wannan labari. Shugaba Jammeh na
Gambia dai yace shi ba matsoraci bane. Yace babu wanda ya isa ya karbe matsayin
sa sai Allah madaukaki. Shugaba Jammeh yace su Buhari sun gama yanke hukuncin
cewa sai ya ajiye mulki tun kafin su gana, yace to ba wanda ya isa.
Shugaban Kasar ta Gambia, Yahaya Jammeh
dai yayi amai ya lashe; da farko ya amice da sakamakon zaben da ya fadi, daga
baya kuma Shugaban Kasar yace faufau bai yarda ba. Jammeh ya fi shekara 20 yana
mulki.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment