– Wani karamin yaro dan shekara 11
ya kai karar Shugaban Kasa Kotu
– Yaron na karar Shugaban Kasar da wanke
kalaman sa, ya shanye
– Kotu ta dakatar da karar har zuwa
wani lokaci
Wani
karamin yaro ya kai Shugaban Kasar Pakistan Kotu inda yake karar Shugaba
Mamnoon Hussein da satar jawabin sa. Wannan yaro ya bayyana cewa shi ya rubuta
jawabin da Shugaban Kasar ya kama ya wanke, ya shanye, ya zuba tamkar nasa.
Wannan
yaro mai suna Muhammad Sabeel Haider yace shi ya rubuta jawaban da Shugaba
Mamnoon na Kasar yayi aman su. Yanzu haka dai wannan yaro ya maka Shugaban
Kasar kara a Babban Kotun Islamabad.
Mahaifin
Yaron, Naseem Abbas Nasir ne ya shigar da wannan kara a madadin dan sa mai
shekara 11 da haihuwa. Yaron yace shi ya rubuta jawabin domin tunawa da MA
Jinnah wanda ya kirkiri Kasar Pakistan.
Yaron
yace wani ne ya saci takardar ba tare da ya sani ba. Kamar yadda Jaridar
Express Tribune ta rahoto, yanzu haka Alkali Aamer Farouk ya dakatar da wannan
kara tukuna. Haidar yace an fada masa cewa za ayi amfani da jawabin nasa, amma
cewa aka yi wata Yarinya ce za tayi ba Shugaban Kasa ba.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment