Thursday, February 2, 2017

Amarya ta mutu bayan mako uku da aure


 Wata Amarya ta rasu makonni uku bayan an daure mata aure


– Amaryar ta rasu tana da juna biyu


Asali ma dai ta rasu ne bayan nakuda





Wani abin tausayi ya faru kamar yadda muka karanto a shafin Facebook. Wata Amarya dai tace ga garin ku nan, duka-duka ba ayi wata guda da yin auren ta ba. Wannan Amarya dai ta rasu jim kadan bayan an daura auren ta.

Wata kawar Amaryar mai suna Princess Nkiru ce ta bayyana haka yayin da ta ke mata ta’aziya a shafin ta na Facebook. Nkiru Momah tace dama can Amaryar tana da juna biyu, sai ga shi ta cika wajen haihuwar ‘da.

Kawar Marigayiyar tana mai kokawa da jimami da ce: ‘Dama na kwarai ba su dadewa.’ Har yanzu dai tana jin abin kamar a mafarki. An daura auren wannan Budurwa mai shekaru 23 a Watan Disamba, ta kuma haihu a Ranar 11 ga Watan Junairu, sai dai jim kadan bayan nan ta ce ga garin ku nan.

Haka kuma kwanaki dai wani Ango daga Garin Katsina ya rasu shi ma ba a dade da daura auren sa ba. Allah ya bada ikon hakuri. 



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...