Thursday, February 2, 2017

An gano maganin Kanjamau a Najeriya



– An gano maganin cutar nan ta Kanjamau a wata Jami’a da ke Najeriya


Farfesa Maduike Ezeibe na Jami’ar Michael Okpara ta Jihar Abia yayi wannan bincike


Shugaban Makarantar ya bayyana haka a jiya



Idan dai ta tabbata Najeriya za tayi kudi da wannan magani


Bayan shekara da shekaru ana bincike wani Farfesa mai suna Maduike Ezeibe a Jami’ar koyon aikin gona ta Michael Okpara ya gano maganin cutar nan da ta gagari mutane watau Kanjamau. A Turance kuma ana kiran ta HIV wanda ke zama AIDS idan ta rika.

Shugaban Jami’ar da ke Garin Umudike na Jihar Abia ya bayyana haka bayan ya tara manema labarai. Farfesa Francis Otunta yayi ikirarin cewa wani Malamin Makarantar ya gano maganin cutar da ke karya garkuwar jiki.

Farfesa Maduike Ezeibe da yayi wannan bincike dai yayi bayanin matakan da ya bi, da kuma sakamakon da ya samu. Yayi amfani da sinadarin Aluminium Silicate da kuma Magnesium Silicate. Sai dai abin da ban mamaki musamman dai tun da Farfesa Ezeibe Likitan dabbobi ne, ita kuma Kanjamau garkuwar jikin Dan Adam ta ke karyawa.

Kwanaki Jaridar Huffington Post ta rahoto cewa yanzu haka an samo maganin Kanjamau kuma har an yi wa wani ma’aikaci a Kasar Birtaniya magananin wannan cuta, kuma ya warke.


[NAIJ Hausa]

2 comments:

  1. ALLAH YAQARA KAWO MAFITA

    ReplyDelete
  2. DAN ALLAH YI GAGGAWAR FIDDA MAGANIN HIV
    DOMIN JAMA A NA CIKIN WANI HALI
    OUT MEDICINE HIV EMERGENCY PLEASE
    DAN ALLAH ATAUSAYA WA RAYUWA

    ReplyDelete

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...