Wednesday, February 8, 2017

An kara kama tsohon Gwamna kafin ya bar Kotu



Tsugune ba ta kare ba: An kara kama tsohon Gwamna kafin ya bar Kotu




Hukumar EFCC ta dai rutsa tsohon Gwamnan Katsina Barista Shema


Da alamu EFCC ta kara damke Shema da wani sabon laifi kafin ya bar Kotu


Ana binciken tsohon Gwamnan da laifin satan kudin al’umma




Tsohon Gwamnan Jihar Katsina Barista Ibrahim Shema dai yana ganin ta kan sa. Don kuwa da alamu Hukumar EFCC ta kara damke sa bayan an tashi daga wata shari’a da aka yi da shi a kotu kamar yadda Jaridar Daily Trust ta rahoto.

Yayin da ake shirin barin kotun, Jami’an Hukumar EFCC suka dura motar tsohon Gwamnan suke nemi ya biyo su, su ka kuma tuka motar sa a baya. Jaridar Daily Trust ce dai ta kawo duk abin da ya faru. Mai magana da yawun tsohon Gwamnan dai yace ba kama sa aka yi ba, tuni dai an daga shari'ar sai nan da mako kusan biyu.

Dama can Hukumar EFCC ta nemi a kama tsohon Gwamnan a rufe a gidan yari, hakan zai sa ba za a neme sa a rasa ba a ko da yaushe. Jami’an ‘Yan Sanda dai sun kora Jama’a da ke kokarin zagaye kotun.

Tun kwanaki dai aka gurfanar da Tsohon Gwamnan na Jihar Katsina Barista Ibrahim Shehu Shema a gaban Babban Kotun Jihar da ke cikin Garin Katsina. Shema ya zargi Gwamnatin APC da makarkashiya, sai dai Gwamna Masari yace Shema ya ji da kan sa.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...