Thursday, February 2, 2017

Wani matashi ya rataye kan sa a Kano



 Wani matashi ya kashe kan sa Garin Kano


– Wannan abu ya faru ne a Karamar Hukumar Gezawa


Ko me ya kawo wannan? Duniya ce ta masa zafi




Mun samu labara daga Jaridar Daily Trust cewa wani matashi ya rataye kan sa har Lahira a Garin Kano. Har yanzu dai ba za a iya cewa ga dalilin da ya sa wannan matashi ya aikata wannan mugun abu ba.

An dai gane wannan matashi mai suna Nura kuma har a lokacin da aka samu wannan labari kafafun sa na lilo a bisa bishiyar sa ya rataye kan sa. Matashin ya rubuta sunan sa ne a wurin kafin ya kashe kan san.

Wannan abu dai ya faru ne a Garin tsamiya da ke cikin Karamar Hukumar Gezawa na Jihar Kano. Wanda yake wurin yace babu wanda ya san mai yayi wa wannan matashi zafi, sai dai aka iske gawar sa tare da casbaha da riga da wasu komatsen sa.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...