– Mai magana da bakin shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi karin haske
– Femi Adesina yace ko shi bai yi magana da Buhari ba a
Landan
– Sai dai Adesina yace yana zantawa
da na-kusa da shugaban kasa
Mai
magana da bakin shugaban kasa Femi Adesina yayi karin haske game da rashin
lafiyar shugaban kasa Muhammadu Buhari da ke Landan tare da kuma bayani a kan
ranar da shugaban zai dawo. Jaridar Sahara Reporters dai tace Buhari na iya kara watanni hudu nan gaba a Landan.
Femi
Adesina a wata hira da yayi a talabijin yace ko shi kan sa bai yi magana da
shugaban kasar ba, sai dai ya kan yi magana da na-kusa da shi din. Adesina yace
yak an tattauna da wadanda suke tare da shugaba Buhari a can Landan.
Mai
magana da bakin shugaban kasar yace shugaba Buhari zai dawo kafin ma lokacin da
ake tunani. Adesina ya kuma soki wasu da ke ta kara ruruta maganar tare da
daura laifin tabarbarewar kasar bisa kan tsohon shugaba Jonathan.
Babban
Lauyan nan na kasa Femi Falana SAN ya soki shugaba Muhammadu Buhari game da
al’amarin rashin lafiyar sa. Falana yace ya kamata ace ‘Yan Najeriya sun san
halin da shugaban su yake ciki.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment