Mukaddashin shugaban kasa
Farfesa Yemi Osinbajo ya shirya farfado da tattalin arzikin Najeriya cikin
watanni biyu. Najeriyar dai ta samu durkushewar tattalin arziki a a bara.
Farfesa Osinbajo ya
kulla niyyar shawo kan matsalar tattalin arzikin Najeriya cikin kankanin
lokaci. Shugaban rikon kwaryar dai zai cin ma wannan burin ne ta hanyar saukake
harkar kasuwanci a kasar.
Yanzu haka an nada wani
kwamiti wanda shi mukaddashin shugaban kasar yake jagoranta mai suna PEBEC
wanda zai kawo sa’ida wajen harkar kasuwanci a Najeriya. Hakan zai taimakawa
kananan ‘yan kasuwa na kasar ya kuma habaka tattalin arziki cikin kwanaki 60.
Ana so dai duk wani dan kasuwa da zai zo Najeriya da hajar sa ya kammala kamai
cikin ‘yan sa’o’i.
Jiya ne shugaban rikon
kwaryar ya dura filin jirgin saman Legas ba tare da tsammani ba inda ya rika
bincika abubuwa da kan sa. Gwamnati na kokarin ganin Najeriya ta shiga sahun
kasar da kasuwanci ya ke da sauki ba tare da wahala ba, wannan zai taimakawa
tattalin arzikin kasar.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment