– Tsohuwar Uwargidan Najeriya Patience Jonathan za ta tsaya
takara
–
Madam Patience Jonathan za ta nemi ta tsaya takara a zaben 2019
– Watakila
Misis Jonathan za ta tsaya takarar Sanata
Da alamu tsohuwar uwargidan
Najeriya Madam Patience Jonathan za ta nemi tsayawa takara a zabe mai zuwa.
Mijin na ta Dakta Goodluck Ebele Jonathan dai yayi mulki na shekaru biyar a kafin
Muhammadu Buhari ya kada sa a zabe.
Patience Jonathan na shirin
neman kujerar Sanata na Jihar Ribas a zabe mai zuwa na 2019 kamar yadda mu ke
samun labari. Wannan labari dai ya jawo ka ce-na ce daga bakin mutane da dama
na Kasar.
Misis Jonathan na iya
tsayawa takarar kujerar Sanatar Mazabar Gabashin Jihar Ribas. Asali dama Madam
Jonathan mutumiyar Jihar Ribas din ce. Idan dai har tsohuwar Uwargidan ta tsaya
takarar, ba mamaki za ta samu nasara, don ko Gwamnan Jihar mutumin ta ne.
Idan ba a manta ba can Jam’iyyar
APC ta kai karar Madam Jonathan din a gaban Kotun Duniya ICC. APC tace Uwargida
Patience Jonathan tayi kokarin tada rikici yayin yakin neman kujera da kalaman
ta a wancan lokaci na zaben shekarar 2015.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment