Tuesday, February 21, 2017

Kiristocin Katsina sun yi wa Buhari addu’a


– Kiristocin Jihar Katsina suna ta addu’a domin ubangiji ya ba Buhari lafiya


– Kungiyar CAN dai ta fara fara azumi da salloli domin shugaban kasar


Shugaba Muhammadu Buhari yana Ingila tun-tuni




A Jihar Katsina mahaifar shugaban kasa Muhammadu Buhari Kiristoci ne suka shiga addu’o’i dare da rana domin Ubangiji ya ba shugaban kasar lafiya. Kiristocin dai sun tashi ne da azumi da kuma addu’o’i domin shugaban kasar ya dawo aiki.

A Jiya Litinin dai Kungiyar CAN ta Kiristoci suka tashi da niyyar azumi har na mako guda domin Buhari. Kungiyar dai tana da ‘Ya ‘ya kusan 65,000 a Jihar Katsina. Kamar dai yadda muka samu labari daga Jami’an NAN masu dillacin labarai.

Kiristocin za su yi addu’a ne na musamman a manyan Cocin da ke Jihar, kamar su Cocin da ke Kofar Kaura da dai wasu da ke cikin gari. Kiristocin suka ce addu’ar su shugaba Buhari ya samu sauki ya dawo ya cigaba da aikin gyaran da ya faro.

'Yan Kungiyar Jama'atu Nasril Islam dai su ma sun dage da yi wa Shugaba Buhari addu'a. A Jihar Borno kuwa, sai sauke Al-Kur'ani ake yi. 



[NAIJ Hausa]




No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...