Friday, February 17, 2017

Koci Arsene Wenger yana ganin uwar-bari


Bayern Munich ta tarwatsa Arsenal a Gasar Champions League


– Wasu suna ganin ya kamata Koci Wenger ya bar Arsenal


– Manyan ‘Yan wasa na iya barin Kungiyar




Kocin Kungiyar Arsenal watau Arsene Wenger na fuskantar barazana da kalubale bayan Kungiyar sa ta kwashi kashin ta a hannun Bayern Munich shekaran jiya. Bayern Munich din dai ta koyawa Arsenal darasi da ci 5-1.

Wasu suna ganin ya kamata Kocin ya tattara kayan sa ya bar Kulob din don kuwa duk shekara Arsenal din ba ta kai ko ina a Gasar. Wannan ne dai shekara ta 6 da ake yi waje da Arsenal din a wannan zagayen.



Arsenal ta kwashi kashin ta a hannu 

An samu rahoto cewa dan wasan gaban Kungiyar Lucas Perez na shirin tashi ya bar Arsenal din saboda karancin buga wasanni. Da alamu dai Manyan ‘Yan wasa irin su Alexis Sanchez ba za su cigaba da taka leda a Kulob din ba.

Haka Kungiyar Barcelona ta sha dan banzan kashi hannun Kungiyar PSG ta Faransa a Gasar na UEFA Champions League. Kungiyar PSG din dai tayi wa Barcelona kaca-kaca ne a filin wasan ta da ke Garin Paris. An fara tunani za a maye gurbin Koci Luis Enrique da Ronald Koeman.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...