Wednesday, February 8, 2017

An shiga uku: An sace ‘Yan kasar waje a Najeriya


An sace wasu baki ‘Yan wata kasa a Najeriya


– Bakin da aka sace dai mutanen kasar Rasha ne da Kasar Ukraine


– Wannan abu ya faru ne a Yankin Neja Delta






Mun samu labari cewa an sace wasu baki ‘Yan kasar waje a cikin Najeriya. Wannan abin kunya dai ya faru ne a Yamkin Neja-Delta mai arzikin mai a kasar.

An dai sace har mutane 7 wadanda duk ‘Yan kasar Rasha ne sannan kuma da wani mutum guda tak dan kasar Ukraine mai makwabtaka da Rasha. ‘Yan fashin kan teku ne dai suka sace bakin a kusa da Garin Brass da ke Yankin Kudu-maso-Kudu na Kasar.

Kafar yada labarai na kasar Rasha mai suna TASS ta sanar da wannan labari. ‘Yan fashin kan tekun dai sun kai hari ne ga kirgin da ya kwaso ‘Yan kasar Rashan a wani Yanki mai arzikin mai. An yi musayar wuta tsakanin ‘yan fashin da masu gadin jirgin. Jami’an Soji dai ta maida martani kwakkwara game da harin.



No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...