Tuesday, February 21, 2017

An sace wani babban Soja a Legas


– An sace wani babban Jami’in Soja a Garin Legas


– A jiya ne dai aka nemi wani Laftanan Soji aka rasa


Babu mamaki masu garkuwa da mutane suka yi gaba da shi





A jiya Litinin ne aka nemi wani babban Jami’in Sojan Najeriya aka rasa a Garin Legas. Wannan abu dai ya faru ne a Yankin FESTAC da ke Garin Legas da yammacin jiya. Ana zargi masu garkuwa da mutane ne suka sace Sojan.

Duk da cewa kwanan nan Gwamna Ambode na Jihar ya shigar da dokar harbe duk wanda aka kama yana satar mutane da alamu wasu ba su koyi hankali ba tukun. Wasu bata-gari ne dai suka kai hari ga Rundunar Sojin yayin da suke wucewa, bayan nan aka nemi wani Soja aka rasa.

Yanzu haka an shiga neman wannan Soja da aka bayyana da Laftana Diya a Yankin na Unguwar FESTAC, Sojoji da sauran Jami’ai sin hargitsa wurin da harbe-harbe da sauran cikin bacin ran ‘dan uwan su da suka nema suka rasa.

Kwanaki ne kuma Mutanen Garin Agatu na Jihar Benuwe su ka tsokano tsuliyar dodo idan har ba ayi wasa ba, don kuwa sun kashe wani Sojan Najeriya kwanan a wata hatsaniya da aka yi tsakanin mutanen Garin da Jami’an tsaro. Sai dai sun nemi a yefa masu kuskuren na su.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...