Wednesday, February 15, 2017

Kotu ta ba gwamnati damar karbe kudin Andrew Yakubu


Hukumar EFCC ta gano kusan Dala Miliyan 10 a wani gida na Andrew Yakubu


Tsohon Manajan NNPC Andrew Yakubu ake zargi ya saci wadannan kudi


Yanzu haka Kotu ta bada dama Gwamnati ta karbe wannan kudi




Wani babban Kotun Tarayya da ke Garin Kano ya bada dama Gwamnatin tarayya ta rike makudan kudin da aka samu daga gidan Tsohon Manajan Kamfanin main a Najeriya watau NNPC Andrew Yakubu.

Hukumar EFCCta samu wasu mahaukatan kudi kusan Dala Miliyan 10 a gidan tsohon Manajan Kamfanin NNPC din na kasa. Andrew Yakubu dai yayi wuf yace duk kyaututtuka ne aka rika kawo masa lokacin yana Ofis. Yanzu haka Kotu ta bada dama Gwamnati ta karbe wannan kudi.




Alkali mai shari’a Zainab Abubakar ta bada umarni a mika wadannan makudan kudi da ke hannun EFCC zuwa Gwamnatin tarayya. Kudin dai sun kai Dala Miliyan 9.8 da kuma wasu Foun £74,000.

Shugaban Hukumar EFCC dai ya jinjinawa Jami’in da ya bankado wannan kudi watau Adamu Dan Musa a Unguwar Sabon Tasha da ke Kaduna. Ibrahim Magu ya jinjinawa Ma’aikatan sa da irin wannan kokari da suka yi.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...