Tun tafiyar shugaba
Muhammadu Buhari kawo yanzu mukaddashin shugaban kasar Yemi Osinbajo ya dauki
matakai da ayyuka da dama a kasar. A wani nazari da muka yi, mun jero manya
daga ciki
Yanzu haka dai Farfesa Osinbajo ke rike da Najeriya ya
kuma yi ayyuka tafiyar shugaba Buhari na a-zo-a-gani. Kadan daga ciki su ne
sauyi da aka gani a tsare-tsaren harkar kudin kasar daga CBN. Farfesa Osinbajo kuma ya
shiga lungunan Neja-Delta domin kwantar da rikicin da ke Yankin.
Mukaddashin shugaban
kasa Farfesa Yemi Osinbajo ya saki kudin wasu manyan kwangiloli a Kaduna da
Legas wancan makon bayan taron Majalisar FEC. Haka kuma Shugaban rikon kwaryar ya
ci burin gyara tattalin arzikin Najeriya ta hanyar saukake harkar kasuwanci a
kasar cikin watanni biyu.
Tun hawan sa dai ya
nada Kwamiti domin ya ji dalilin da ya sa farashin abinci ya tashi a Najeriya.
Farfesa Osinbajo ya kuma gana da shugabannin Majalisa ba sau daya ba, ba sau
biyu ba a game da harkar kasafin kudin wannan shekarar.
Osinbajo ya kuma
rattaba hannu a wasu kudirori da Majalisar ta aiko masa yayin da kuma yayi
mursisi yayi watsi da wasu kudirorin tare da bayyana dalilan sa. Har a kasar
waje dai ana ta kawo ziyara ga shugaban kasar na rikon karya inda shi ma ya
taka har kasar Gambia wajen nadin sabon shugaba Adama Barrow.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment