Monday, February 6, 2017

Ana kukan rashin kudi a mulkin Buhari


Ma’aikatan Gwamnati sun koka da halin da ake ciki a Najeriya


Ana fama da masifan rashin kudi


Shugaba Buhari yana yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya





A wani bincike da wata Jarida tayi an gano cewa Ma’aikatan Najeriya sun koka da irin halin da ake ciki na rashin kudi a Najeriya a wannan mulki na shugaban kasa Muhammadu Buhari. Abin dai har ya kai ga manyan motoci hannun Ma’aikata amma babu kudin zuba masu mai.

Ma’aikatan Najeriya dai sun saba cuwa-cuwa watau ha’inci to yanzu ta kai kowa yana dogara ne da dan albashin sa. Hakan dai ta sa Jama’a na ta cire ‘Ya ‘yan su daga manyan Makarantu masu mugun tsada. Ana dai ganin cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya hana mutane damar da suke samu a da.

A lokacin baya Najeriya ta samu makudan kudi daga bangaren mai, hakan ya sa aka yi ta facaka, sai dai fa yanzu abubuwa sun canza tun zuwan Muhammadu Buhari. Yanzu haka an maida asusun kudin Kasar zuwa biai daya watau TSA wanda wannan ya kawo sauyi kwarai da gaske.

Wadanda suka saba barna da kudi sun shiga cikin wani hali da ba su saba ba, wasu ma dai na da wasu mutanen dabam a karkashin su. Yayin da kudin sata yayi wuya, sai kowa ya zama kaffa-kaffa. Ko ya za a kare da Yaki da rashawar da wannan Gwamnati ta dauko?



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...