Wednesday, February 22, 2017

‘Yan Najeriya sun yi ca a kan Sarkin Kano


– Mutane sun fara tofa albarkacin bakin su game da maganganun Sarki Sanusi II


– Sarkin Kano yace za a hana talaka yawan aure a kasar sa


Wannan maganar ta jawo ce-ce-ku-ce a Gari




Kalamai da kudirin Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II sun jawo ce-ce-ku-ce a Gari yanzu haka a cikin mata. Mai Martaba Muhammadu Sanusi II yace za a hana talaka tubus kara auren mata a kasar sa.

A wata hira da Hukumar dillacin labarai na kasa watau NAN tayi da wasu mata a Maiduguri, wasu sun bayyana cewa hakan abu ne mai kyau yayin da wasu matan kuma suka ce gaba daya bai dace a kawo irin wannan doka ba. 

A wani bincike da Jaridar Daily Trust tayi wasu matan sun nuna cewa sun yi na’am da Sarki suka nemi kuma a mara masa baya, wasu matan dai sun ce hakan na iya kawo matsala ga matan da ke neman mazaje ido rufe.

Sarkin dai yace za a hana wadanda talauci ya masu katutu aure barkatai wanda a karshe suke gaza kula da ‘ya ‘yan su, Sarkin yace wannan ke kawo ‘ya ‘ya a Gari wadanda suke zama ciwon kai ga al’umma. Wasu dai sun ce ko ya za iya da tarin ‘yan matan da ke Gari?



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...