Wednesday, February 22, 2017

Rashin wutan lantarki ke hana mu aiki-Minista


– Ministan harkokin mata tace sai su fi makonni 5 ba tare da wutan lantarki ba


– Aisha Jummai Alhassan ta bayyana haka ne a gaban majalisa


Rashin wuta dai ya zama ruwan dare a Najeriya





Da alamu dai rashin wutan lantarki ya zama ruwan-dare a Najeriya, a jiya ne Ministar harkokin mata Aisha Jummai Alhassan tace har Ma’aikatar ta sai a shafe fiye da wata day aba tare da kiftawar wuta ba.

Mama Taraba kamar yadda aka san ta, tace rashin wuta ne ya hana ta kawo takardun da ake bukata wajen tattaunawa da kuma tsefe kasafin ma’aikatar na wannan shekarar. Aisha Alhassan tace rashin wuta ne ya addabe su a Ma’aikatar wanda a wani lokaci sai a kusa makonni 6 babu wutar lantarki.

Ministar tace dole ita da Sakataren Ma’aikatar suka hada kudi daga aljihun su suka saye man da aka yi amfani da shi a Injin janareto. Ministar tace rashin wuta ne dai ya hana ta zuwa ta kare kasafin ma’aikatar ta a Majalisa, tace ba za a kara yin hakan ba. 

Haka dai kwanaki aka dauke wuta yayin da ake tantance Jakadun kasar a cikin Majalisar Dattawan Kasar. Rashin wuta dai ya zama ruwan-dare.


[NAIJ Hausa]







No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...