Tuesday, February 7, 2017

FIFA ta hukunta Najeriya


Hukumar kwallon kafa na Duniya FIFA za ta cigaba da hukunta Chris Giwa


– Dama can Chris Giwa da wasu suna cikin masu laifi


– Chris Giwa na rikici da Shugaban kwallo NFF na Najeriya




Kungiyar FIFA ta kwallon kafa na Duniya za ta cigaba da hukunta wasu Jami’an kwallon kafar Najeriya watau NFF. FIFA tace har yanzu ba ta yafewa Chris Giwa da sauran Jami’an Najeriya da ta samu da laifi ba.

Kungiyar FIFA ta Duniya ta kama Chris Giwa da wasu da rikicin shugabancin kujerarar NFF na Najeriya a baya. Sauran Jami’an da aka hukunta sun hada da Muazu Suleiman, Johnson Effiong, Fema Sani da Yahaya Adama.

Idan dai ba a manta ba Chris Giwa ya kalubalanci shugaban kwallon kafan Najeriya NFF watau Amaju Pinnick yace sam shine shugaba ba wani ba. Bayan nan ne FIFA ta Duniya ta takawa Giwa da mukarraban sa burki, aka kuma hana su shiga kowace irin harka ta kwallon kafa a Duniya.




 [NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...