– Wai a bar tuna-baya Inji Hausawa Mahaukaci ya zama Sarki
– A Kasar Zimbabwe wata mai-zaman kan ta ta zama
Ministar yada labarai
– Ministar
ta roki a bar tuna baya
Wata Minista a Kasar
Zimbabwe ta nemi ‘Yan Kasar su bar tuna lokacin baya, Ministar dai ta taba
zaman kan-ta a baya, tace amma yanzu ai komai ya wuce, kuma kyaun ta a dai bar
tuna baya.
Minista Kampamba Mulenga ta
yada labarai a Kasar Zimbabwe tace abin da za ayi la’akari da shi yanzu shine
aikin ta a matsayin Ministan yada labarai. Ministar tace yanzu ta canza ta kuma
ajiye wancan aiki a gefe.
Ministar tayi wannan magana
ne inda ta ke nuna takaicin ta da wasu da ke kiran ta da sunan da aka san ta a
da. Kampamba Mulenga ta cewa Mutanen Kasar yanzu ta canza ya kamata kuma
al’umma su ba ta girman ta. Kafin ta zama Minista a Gwamnati dai kamar yadda
Daily Post ta rahoto kowa ya san ta a matsayin mai zaman kan ta.
A farkon wannan Watan tsohon
shugaban kasa Dr. Goodluck Ebele Jonathan ya gabatar da jawabi a gaban Majalisar
Amurka inda aka gayyace sa domin yayi magana game da matsalolin Najeriya
musamman rikicin addini da sauran su.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment