Monday, February 6, 2017

EFCC ta karbe gidan wani tsohon Gwamna


Hukumar EFCC ta karbe gidan tsohon Gwamna Isa Yuguda


Wata Kotu ce ta ba EFCC damar karbe kayan tsohon Gwamna na Bauchi


Ana binciken Yuguda da laifin satan dukiyar Jama’a




Hukumar EFCC mai yaki da cin hanci da rashawa ta karbe wasu kaya na tsohon Gwamnan Jihar Bauchi Isa Yuguda. Wannan ya biyo bayan wani babban Kotu da ke Abuja ta ba Hukumar damar hakan.

Yanzu haka dai Hukumar ta EFCC ta karbe gidan tsohon Gwamna Yuguda da ke Unguwar GRA na Bauchi. Wani Jami’in Hukumar EFCC yace za a rike gidan ne na wani dan lokaci kafin a kammala bincike.

Ana zargin tsohon Gwamnan da laifin satar kudin Jama’a da wuce gona da iri lokacin yana kan kujera. Alkali J. Tsohon na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba Hukumar EFCC damar karbe kayan tsohon Gwamnan a wancan makon.






[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...