–
Manyan malaman Kano sun yi shugaban kasa Muhammadu Buhari addu’a
– Sheikh
Daurawa yace shugaba Buhari na bukatar addu’a
–
Gwamna Ganduje yayi magana da shugaba Buhari
Kusan duk wani babban malami yana cikin gidan
gwamnatin Jihar Kano jiya inda aka yi wa shugaban kasa Muhammadu Buhari addu’a.
Malaman sun yi wa shugaban addu’ar karin lafiya ya samu ya cigaba da mulkin
kasar nan.
Manyan malami irin su Malam Aminu Daurawa, Sheikh
Isiyaka Rabi’u, Sheikh Muhammad Nasir Adam, Sheikh Adam Suleiman da sauran
Shehunnai suka halarci gangamin inji Jaridar Vanguard. An dai ta karatun
Kur’ani domin shugaba Buhari ya samu waraka.
Shugaban Hisbah Sheikh Daurawa yace shugaban kasar na
bukatar lafiya domin ya cigaba da tafiyar da al’amurar kasar nan tare da goyon
bayan Jama’a. Gwamna Abdullahi Umar Ganduje yayi magana kai-tsaye da shugaban
kasar inda ya bayyana yadda Jama'a ke ta masa addu'a, shugaba Buhari yayi matukar
godiya ga mutanen a wayar tarho.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment