Tuesday, February 7, 2017

Likitocin Asibitin Jami’ar ABU ta Zariya sun tafi yaji


Likitoci sun shiga yajin-aikin a Asibitin Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya


Yajin aikin ya shafi sauran Malaman Asibiti


Ma’aikatan sun ce babu ranar dawowa




Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa Malaman Asibitin Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya sun shiga wani yajin aiki jiya. Kwanan ne dai aka sake bude Asibitin bayan an kaddamar da wasu gina-gine an kuma canza masa suna.

Ma’aikatan dai wanda suka hada da Likitoci da sauran Malaman Asibiti sun tafi yajin ne a jiya wanda kuma suka ce babu ranar dawowa har sai Hukuma ta duba kukan su. Ma’aikatan dai sun ce Hukumar Jami’ar ta gaza biya masu bukatun da suka yi yarjejeniya.

Shugabannin Kungiyoyin Ma’aikatan Asibitin guda hudu dai suka rattaba hannu a kan takardar da ke sanar da cewa Ma’aikatan Asibitin za su koma yajin aikin su. Wani ya bayyana mana cewa ya je Asibitin amma ba a aiki dole ta sa ya dawo gida. Har yanzu dai Jami’ar ba tace uffan ba.

Haka dai kwanaki Likitocin Asibitin koyan-aiki na Jami’ar dai ta Ahmadu Bello suka shiga yajin-aiki na din-din-din. Kungiyar Likitocin Asibitin da ke Shika, sun shiga yajin aikin ne bayan an gaza biya masu bukatun su.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...